Arubuce Ta Ke Hausa NovelHausa Novels

Arubuce Ta Ke 76

Sponsored Links

Page 76

Tunda akayi sallar magariba bai motsa ba a masallacin,yaci gaba da zama yana sauraren masu karatu dakeyi tsakanin magariba da isha’i,idanunsa a lumshe amma ita yake hangowa a ciki,yasan dai yau zaisha daaru da qorafi,to amma hakan yafi masa sauqi akan abinda zaije yazo,a yanayin da yake ciki yasan ko hafsat saidai idan zata nuna juriya ne kawai,bawai don qarfinta zai iya dauka ba.

Har aka gama karatun aka yi sallar isha’i ba abinda ya canza,ya kalli agogo tara saura na dare,yasan a yanzun tana shirin kwanciya saboda akwai makaranta gobe,sai ya tashi yayi Shafa’i da wutiri sannan ya baro masallacin,bai koma gidan ba sai daya biya ya siya fruit.

Tana lafe cikin kujera tana qananun hawaye,ga kukan mage daketa zarya yau tsakanin sassansu da ainihin main gidan,ya tura qofar da qaramar sallama maqale a bakinta,ga mamakinsa sai ya hangeta cikin kujerar,yayin da ganinsa ya bata qwarin gwiwar miqewa da gudu tayo wajensa,tana zuwa ta fada jikinsa ta sakar masa kuka

Lips dinsa ya cije,ya dora hannunsa saman sumarta dake tsole masa idanu tun shigowarsa ta dazu yana shafa sumar daga saman kanta har zuwa inda jelar kalbar ta tsaya,bakinsa ya kasa furta komai,sabosa yadda komai ya dawo masa sabo bayab kasancewarta cikin jikinsa.

Sun jima a haka,yanata karbar feelings yana mazewa har zuwa sanda ta lafa da kukan

“To mene na kukan?” Cusa kanta tayi a qirjinsa,itama qamshinsa yana qayatar da ita,sai data tura baki gaba kamar yana kallonta sannan tace

“Ba kaine ba,na dade inata shan wahala,nayi maka girki kuma daga shigowa saina nemeka na rasa”

Murmushi ne ya subuce masa,ya hadiyi yawu da qyar sannan yace

“That’s all?” Kai ta gyada masa a hankali

“To ya isa,yanzu bari nayi wanka nazo naci abincin,ai bance bazanci ba ko?” Hakan daya fada yayi mata dadi,ta rakashi dakin ta hada masa ruwan wankan da kanta,amma sanda taga ya fara balle botiran rigarsa saita miqe zata gudu.

Hannu daya yasa ya dawo da ita gabansa,ya futa tsaho sosai,saiya sake janyota zuwa jikinsa suka hade waje daya,ya bata saman qafafunsa ya taka,hakan ya qara mata tsaho,yana riqe da ita da hannu daya,daya hannun kuma yana cire maballan.

Saura hudun na qasa,saiya saki,ya kamo hannunta a tausashe ya dora akan qirjinsa

“Qarasamin” ya fada yana saka daya hannun nasa ya zagaye bayanta dasu,hakan ya bata damar tsaiwa sosai,saidai dukka hannayenta biyu rawa suke,fatanta kawai ta cika umarnin mommmy data gaya mata duk abinda yace yanaso daga yau ta tabbatar tayi.

Fuskarta yaci gaba da qarewa kallo sanda taje cire masan,tun daga cikakkiyar girar idonta,qaramin lallausan kabbanta,tana da wani irin kyau me sanyi da tsayawa a rai,duk da har yau yaga alamar batasan wannan baiwar da take da ita ba.

Duk second daya da zasu qara a haka sake qayatar dashi tsaiwar take,rawar da hannunta keyi yasa ta dauki lokaci kafin ta gama,duk da cewa saman qafafunsa take a tsaye,amma hakan baisa yaji gajiya ba ko kadan

“N…..na gama”ta fada muryarta tana dan rawa,saiya sukunya gishinta yayi kissing dinta,zuciyarsa nata tunzurashi ya zarme amma yana mata waigi,two step back yayi yana sauketa sannan yace

“Thank you” ya furta hade da wani siririn murmushi ya wuce ta saman labbansa,saiya fara zare rigar,ta juya da hanzari ta fita a dakin, murmushi ta qara saki yana girgixa kai,ya dauki towel da widad din ta yiwa waje na musaman ya rataya ya shiga wanka,wannan ya bata damar guduwa daga dakin.

Komai ta shirya masa a table mat,sai data tabbatar komai yayi sannan ta wuce daki ta debo books dinta na makaranta da aka basu assignment ta dawo dasu parlor din,don dama kusan ko yaushe tare sukeyin assignment,saita koma koma ta zauna saman kujera tana jiran fitowarsa,wayarta na hannunta tana chart.

Ba jimawa sassanyan qamshinsa ya soma isowa parlor din,ta daga kai a hankali tana dubansa,yayi kyau cikin wasu light blue din kaya,fuskarsa tayi fayau kamar wanda yayi aikin wahala,saidai yayi fresh ya kuma yi kyau.

Tana murmushi ta miqe tana cewa

“Kazo kaci uncle please” tayi maganar tana karyar da kai gefe,sai ya sakar mata murmushi,komai nata burgeshi yakeyi,duk da tana komai ne ita bilhaqqi da gaske,ya tako a hankali har yanzu jikinsa babu qwari ya zauna.

Tana serving dinsa tana zuba masa surutu, yana daurewa ne kawai yana biye mata, saboda yadda gaba daya qamshinsa ke tafiya da hankalinsa,uwa uba rigar ta mugun fidda surar qirjinta da suka fara cika suna bin girma da jikinta ya fara yi,ta gama zuba komai ta tura masa tana cewa

“Aci a bani mark” kai ya jinjina ya fara diban abincin yana ci,shuru yayi yana jinjina dadin taste dinsa,baisan sunan abincin ba saboda bana hausa fulani bane,amma tako ina ya tafi dashi.

Itakuwa tana zaune gabansa ta tsira masa ido tana jiran jin abinda zai fada,kusan minti biyar shuru,saita fara bubbuga qafafunta

“Uncle….. uncle…..baiyi dadi bane?” Idanunsa ya zube mata ya lumshesu kadan sannan ya jinjina mata kai

“what a wonderful taste!…..na kasa magana ne don kada nayi shirme,I have never eaten food that tastes like this” dadi sosai ya cikata,dariyar farinciki ta kubce mata,saita matso tana dauko pillow zata saka masa a baya tana cewa

“Bari na fara da saka maka waigi kada ka fadi” hakan da tayi ya bawa tudun qirjinta damar gogar jikinsa,nan take ya qware da abincin da yake qoqarin hadiyewa yahau tari.

Da sauri ta tsiyaya ruwa ta bashi tana masa sannu,duk fuskarta ta nuna damuwa qwarai,idanunta sukayi narai narai da hawaye,tayi tsai tana kallonsa gami da jero masa sannu har tarin ya lafa

“Sannu uncle,ko na qaro maka ruwan?” A tausashe ya dubeta,wani kimarta da mahaukaciyar soyayyarta tana ratsashi,he never thought that she would care about him so much duba da qananun shekarunta da kuma yadda wadda ta girme mata ta ninka shekarunta ma ba haka take masa ba.

He wonders how she shows concern for him,ko yaya yayi dare ko ya gaggara cin abinci duka sai tabi ta damu kanta,bare taga alamun bashi da lafiya,saita zauna ta dasa masa kuka har sai yayi da gaske wajen qarfafa jikinsa da nuna mata ya warke,ko iya wannan kulawar ya samu alhamdulillah,ko iya haka ya fuskanci manufar hajiya akan yarinyar…..ko haka aka tsaya ya samu tarin abubuwa da yawa daya rasa daga wacce suka debi shekaru tare,ko a iya wannan ya samu abubuwan da ada baisan namiji yana samu daga wajen matarsa ba,saidai yana buqatar qari…..zuwa lokacin ya fara gano muhimmancinta me girma cikin rayuwarsa,yana son ya maidata tashi…..halak malak……yanason su sake zama.abu daya,yana son dandana mata soyayya mai zaqin da dandanonta bazai iya fita daga halshenta ba,yanason ta zama tasa ta har abada.

Sai data tabbatar ya nutsu sannan ta debe kayan abincin,ta kuma gyara wajen tas yana daga zaune cikin mutuwar jiki yana kallonta,daya daga cikin abinda yake burgeshi da ita,bata yarda tabar waje a hargitse ba.

Dab dashi ta zauna har cinyarta tana gogar tasa,cikin jikinsa ta aike masa da wani saqo me nauyi ba tare data san tayi ba,a kwanakin nan da sabo ke sake shiga tsakaninsu haka take masa,ko meye zatayi tana maqale da jikinsa kamar mage,ya fuskanci ta saba ne tun a gida,tana da son jiki,kuma hakanan dama takewa ummu.

Saman cinyarsa ta dora littafin da hannunta duka,sannan a shagwabe tace

“Uncle….. assignment fa” jikinsa gaba daya ya dauki rawa,yasa hannu cikin zafin nama ya janye hannayen nata duka biyu daga jikinsa,tsoro yadan shigeta ganin yadda ya sauya lokaci daya, muryarta a narke kamar zata saki kuka tace

“Uncle bazaka yimin ba?”kai ya girgiza muryarsa na dan rawa

“No”

“Amma shine ka ture ni?” Ta sake fada hawaye na cika mata idanu,zuba mata ido yayi wani abu na zaga jininsa,tana sake shiga rayuwarsa da wani mugun gudu da kuma gaggawa,bayason tana shige masa a irin wannan situation din da yake ciki,idan taci gaba kuwa bashi da tabbacin abinda zai iya biyo baya

“Banaso kina hawa jikina” kunya ta saukar mata,itace ma ke hawa jikinsa?,sai ta miqe da sauri har tana zubar da litattafan cikin borin kunya tana hawaye ta shige daki.

Da kallo ya bita har ta bace,sai.ya dawo da dubansa nan inda ta tashi yana sauke wawiyar ajiyar zuciya hadi da rufe idanunsa,bazai bita ba don kusancinsu da ita zai iya haifar da komai,ya miqe a hankali ya wuce dakinsa yana jin yadda komai na jikinsa ya daddaure.

Saman pillow ta kifa fuskarta kunya na cikata,me yasa take yawan zama a jikinsa?,itama bata sani ba, yawancin lokuta ma batasan tayi ba banda yanzu daya fada,ta jima a haka tana jin kunyar kanta da kanta kafin ta miqe ta shige toilet,tayi brush ta dawo gaban madubi ta fara shirin kwanciya.

Haka kawai ta zauna ta bata lokaci tana duba duka turarukanta,na gefen kunne na gabobi na matse matsi da sauransu,tana karantawa tana shafawa

“Bari dai na gwada naga da gaske da qamshi” ta fada a sakalce,ita kanta da kanta sai data dinga bin jikinta tana shanshanawa ta lumshe ido

“Hmmmm,aikuwa kullum saina shafa,ashe dai da gaske da qamshi” duka ta gama wannan,saita wuce cupboard dinta ta bude tana ‘yan waqenta,leda ce ta biyota ta fado,a dan tsorace taja baya ta zubawa ledar ido,saita tuna ledar da matar gidan da suke ciki ta bata kyauta ce ranar data fara shiga,ta dauka ledar ta bude tana zazzage kayan ciki.

Murmushi ya subuce mata sanda ta tuna abinda ta cewa abbas randa aka bata kayan,ya zuwa yanzu ta karanta amfani da muhimmancin kayan

“Bari dai na gwada mu gani” ta furta tana dauko daya daga ciki,wine color ce mai wani matsiyacin ado na fararen furanni a jikinta,ta net ce mai wani irin sulbi kamar silk net,ta zura rigar harda pant dinta,sannan ta isa gaban madubi tana canza tafiya.

Dan ihu ta saki tana fidda ido ganin komai nata ya bayyana muraran,ta rufe bakinta za hannayenta tana sake kallon kanta da kanta tare da jin kunyar kanta,saidai ta dade bataga abinda yayi mata maqurar kyau irin rigar ba.

Wani abu ya darsu a ranta,gata gaban uncle abbas,saita fara jujjuyawa yadda ta taba gani a wani littafi tana gwada shine a gabanta.

Kamar jira maqalalliyar magen gidan takeyi ta soma kuka tana kusur kusur jikin window glass dinta,mummunan faduwa gabanta yayi,ji tayi kamar ma ta shigo dakin saboda daya side na window din a bude yake,sai net kawai,ai bata tsaya tunani karo na biyu ba ta kwasa da gudu ta fita a dakin,bata kuma nufi ko ina ba sai dakin abbas cikin mugun tsoro.
[3/17, 1:28 PM] +234 813 343 4840: *H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K’addarata)
*Arewabooks:Huguma*

Leave a Reply

Back to top button