Hausa NovelsNoor Al Hayat Hausa Novel

Noor Al Hayat 14

Sponsored Links

By khaleesat Haiydar_📚✍🏻

14…..

Tsayawa yyi yana kallonta ta shiga parlorn sannan shima ya shiga, kan kujera ta nufa ta xauna, ya karaso bayan ya kulle kofar ya ajiye ledan hannunsa kan center table, sannan ya shiga daki, jinginar da kai tayi da kujera tayi xurfi cikin tunanin da take taji yana kiranta, dagowa tayi da sauri ta gansa tsaye gefenta ya rungume hannunsa, a hankali yace “Na hada maki bathing water a bathroom” sunkuyar da kai tayi, ta mike yana gaba ta bi bayansa xuwa dakin, towel ya dauko ya mika mata, ta karba murya can kasa tace “Thank you” ya juya ya fita dakin, da mouth wash na Listerine ta wanke bakinta, tayi wanka da shower gel, sai kusan bayan minti talatin ta fito daga bayin, bayan tayi ta tsayuwa bakin kofar bathroom din tana tunanin fitowa da towel, bbu kowa dakin sai Hijab dinta da ta gani kan gado, mamaki ya kama ta tayi ta kallon Hijab din, karasawa tayi ta dauka ta koma bathroom din, wanke kayan da ta cire tayi sannan ta sa hijab din ta fito da kayan da ta wanke a bucket, xaune ta gansa a parlor yana rike da remote, kallo daya yyi mata ya dauke kai har ta shigo parlorn, yace “Why did u wash, u still under medication” bata ce komi ba, yace “Na bude maki kofar….” Tace “Da gaske?” Yace “Ehh, ki tafi ki shirya” murya can kasa tace “Nagode” sannan ta wuce tana rike da Hijab din. Sai da tayi sllh snn ta wanke masa towel din a bayinta ta fito ta shirya ta tafi shanya kayan da ta wanke da towel din nasa, kwanciya tayi daki bayan ta gama lkci daya bacci ya dauketa. A hankali ta bude ido jin kamar ana tashinta, ta mike da sauri tana kallon sa, yace “I’ve been knocking and calling since, but…. Taso mu je ki ci abinci” ta girgixa kai tace “Am not hungry bacci nake ji” yace “Noo, baki ci komai ba yau, kuma kinga xa ki sha magani, you have to take something….” Daga haka ya mike yana kallonta, sauka tayi daga kan gadon ta bi sa suka fita parlor, xuba mata abincin yyi ya mika mata ta karba ta fara ci, wayarsa yake ta dannawa har ta ajiye abincin tana yamutsa fuska tace “Na koshi fa” ya kalli abincin sannan ya dau ledan maganin ya ballar mata drugs din ya taso ya mika mata da goran ruwa ta karba, ta sha maganin tana kallon sa yace “Allah ya sauwake” bata iya ta ce komai ba, yace “To ki je ki kwanta, sleep without thought plss” ta gyada masa kai sannan ta tashi ta shiga daki. Bata tashi ba sai kusan biyu da rabi na rana, ta shiga bayi tayi alwala ta fito tayi sllh, tana idarwa ta sake kwanciya. Knocking kofar dakin taji ana yi cikin bacci, ta mike xaune ta sa hijab sannan ta bude kofar, yana tsaye bakin kofar, yace “Have u prayed zuhur?” Ta gyada masa kai, yace “Abinci fa” tace “I am not hungry” ya girgixa kai yace “You are, fito ga abinci na kawo maki sai ki sha magani” daga haka ya juya ya bar wajen, bin sa tayi, yana daga tsaye ya nuna mata abincin kan table, ta karasa ta dauka, tuwon shinkafa ne da miyar vegetable ta gani da ta bude, ta daga kai tana kallon sa, ya daga kafada yace “Yea, a frnd of mine ce ta yi…” Tace “Kai baxa ka ci ba?” Ya girgixa kai da sauri yace “Noo I don’t take heavy foods, I don’t take swallow” murmushi tayi ta dauke kai, ya shafa kai yace “Sbda ke na karbo” tace “Toh ngd” yace “No thanks” plate taje ta dauko a kitchen ta debi abincin, shi dai har lkcn yana tsaye, ta kallesa a hankali tace “Baxa ka xauna ba” shiru ya d’an yi, sai kuma ya karaso ya xauna kan kujerar dake kallon nata yace “So u care” bata ce komai ba ita dai, a hankali ta dinga cin tuwon, duk lkcn da ta daga kai sai sun hada ido, daga karshe bata sake yrda ta dago ba har ta gama cin tuwon ta dau magani ta sha, sai a snn ta sake kallon sa taga kallonta yake still, hade rai tayi ta dauke kai, yyi murmushi yace “Who is Aliyu?” Kallon sa tayi da sauri, kamar yanda shi ma yake kallonta har lkcn, can ta tsuke fuska tace “Ban gane ba” bai sake cewa komai, bayan kusan minti biyar yace “don’t pretend… Is he ur Husband?” xuciyarta na bugawa tace “Nooo” Yana mata wani kallo yace “Ur Ex Husband?” Hade rai tayi sosai cike da masifa tace “Noooo” sai kuma ta mike tana masa wani kallo tace “I know nothing about what u are saying” ya d’an yi murmushi yace “You passed out yesterday at the hospital with the name Aliyu in ur Mouth” shiru tayi tana kallon sa a sanyaye, lkci daya hawaye ya cika idonta, can ta juya ta bar masa parlorn da sauri, kiran ta ya dinga yi har ta shige daki ta xauna kasa ta hade kai da gwiwa ta fashe da kuka, bin ta yyi cikin dakin, ya karaso gabanta ya durkusa a hankali yace “Ohk, I am very sorry Khadijah, may be I shouldn’t have say anything about that, but dole xan yi magana, Billah da xan ga Aliyun nan… Sai na sa ya d’an dani abin da kike ji, I guess he broke ur heart kuma yake kokarin dawowa rayuwar ki yanxu saboda may be selfish reason dinsa, he will regret that duk ranan da muka hadu face to face…. I vow!” ita dai bata ce masa komai ba sai kukan da take, duk jikinta yyi mugun sanyi, mikewa yyi ya fita dakin. Har dare khaleel bai shigo ba, tun da tayi magrib take hade abubuwan da tasan xa ta kai gida, don bata jin xata kara kwana a kasar, gaba daya xaman kasar da karatun ya fice mata a kai, hawaye kawai take duk jikinta a sanyaye, Sudais has always wanted her to be a doctor, ta xo ta samu kan ta a bangaren pharmacy, wanda a yanxu bata jin ma xata ci gaba, domin kuwa ta hakura da karatun, may be some other time she wil be d doctor Sudais wants her to be, to ko ta xama likitan ma what is that adding to her life, wanda take son yi dominsa ya tafi ya bar ta a lokacin ta fi bukatarsa a rayuwarta, baxa ta ce ya gujeta ba, but what’s the difference? Kusan duk daya…. Ta share hawayen idonta ta fito parlor a sanyaye, tsaye tayi tana kallon Khaleel da shigowarsa knn a hankali ta sauke idonta kasa wasu sabbin hawayen na xubo mata, ya karaso kusa da ita yace “Ina xa ki?” Ta juya masa baya tana kkrin ganin bata fashe da kukan dake cin ta ba, a hankali yace “Khadijah” cikin rawar murya tace “Am going back to Nigeria” ya juyo da ita ya xaunar gefen kujera yana kallonta, ya bar ta tayi kukan me isarta, ta hade kai da gwiwa tana sauke ajiyar xuciya, cikin sanyin murya yace “Tell me about you Khadijah” Ta dago tan kallon sa hawaye na sakko mata, sai dai kuma tayi ma kanta alkawarin bayan Sudais bbu wanda xai ji ita wacece, muryarsa ya dawo da ita tunanin da take, yace “I still don’t deserve to know you koh?” Ta sunkuyar da kanta tana goge hawayen dake sakko mata, a ranta kuwa tunani take anya xata iya fadi ma Khaleel ita wacece kuwa, a hankali ta xamo kasa daga xaunen da take kan kujera, ya sakko k’asan shima yana kallon kwayar idanuwanta da suka rine, kife kanta tayi da kujera cikin sanyin murya tace “Ka daina kallona da idon ka” ya d’an yi jim sai kuma yace “Why?” A hankli tace “Bana son irin su” murmushi yayi yace “Da gaske” taki cewa komai, a hankali yace “Toh na daina kallon ki” dagowa tayi suka kara hada ido tayi saurin mayar da kanta jikin kujera, dariya ta basa sai dai bai yi ba ya shafa kansa yana murmushi, murya can kasa yace “Am all ears Khadijah” ta dago kanta tana wasa da dogayen yatsun ta tace “Ohk…..” Wayarsa ya da ya fara ring ya ciro aljihunsa, ta kalli screen din kamar yanda shi ma yake kallo, Jawaheer ne jikin screen din… Yyi silencing wayar ya ajiye a hankali, Tsura ma lallausan carpet din da suke xaune kai ido tayi ko kiftawa babu, cikin sanyayyan muryarta tace “I am an only child… I was raised from a very rich home, I was raised by only my Dad don kuwa ina da shekara uku kachal a duniya mahaifiyata ta rasu….” D’an murmushi tayi wasu sabbin hawaye na taruwa idonta tana kallon Khaleel da ya kafeta da nasa idon….

Who is Khadijah?

Back to top button