Hausa NovelsSakayyah Complete Hausa Novel

Sakayyah 56

Sponsored Links

 

SAKAYAH

 

56

 

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

 

 

“Ki faɗi gaskiya dai ko dai ko dai Magungunan _Aunty Aysha Aliyu Garkuwa_ sun fara aiki ajikin kine dan naji yanda su Aunty Ruƙayya da Aunty Hajara ke tabbatar da kyau da inganci maganin”.

Khausar na gyara kwanciya tace.

“A kin manta ba aiki ba uban aiki suka fara”.

Dariya Asma’u ta sanya tare da faɗin.

“Toh bani na kar zomon ba”….

Cikin sauri ta juya baya tare da rumtse idanunta, tana maganar zuci. haba da gskyar Asma’u inaga harda wannan tsume-tsumen ke ƙara gigitani gashi shima wannan Yah Modibbo duk ya hautsuna min natsuwa da rikitattun idanunsa masu kashe jiki,

da haka bacci ya kwasheta.

 

Washe gari tun da safe akazo akafara shirya Khausar ahaɗa mata wannan ruwan ƙamshin da Zaran ta gama ta fita za’a sake haɗa mata wani aƙalla sai da aka kusan haɗa mata kala bakwai zuwa dare.

kana aka koma na turaren hayaƙi da zai tsumata suma sun kai kala goma yinin wannan ranan haɗa ta akayi wani irin Masifeffen ƙamshi take da Zaran ta tashi awaje ƙamshinta zai bule.

Yayinda tuni kuma an kai mata Set ɗin akwatinanta duk anje anjere a Side ɗin ta…

 

Bayan an idar da sallar Isha’i Jakadiya, Lalla Hafsat, Rahma ne suka shigo falon su Khausar yayin da hannunsu ke riƙe da wata jaka abakin gado Lalla Hafsat ta ajiye kana ta juya ta kalli Khausar tace.

“Ya dai ƙanwata?”.

Khausar na murmushi ta sunkuyar da kanta tare da faɗin.

“Lafiya lau Aunty Hafsat ya gida?”.

Cikin sakin fuska tace.

“Alhamdulillah ya gajiyar biki da hidima mun kasa barinki ki huta ko?”.

Murmushi tayi batare da tace komai ba.

 

Tana zama tace.

“Kiyi haƙuri muɗin ne muna da yawan al’adu dan ma abin ne yazo ahaka an rage saura”.

Murmushi Khausar tayi akaro na biyu ta kuma sunkuyar da kanta.

Kallon Khausar dake wasa da yatsun hannunta tayi tare da cewa.

“Yanzu ki tashi Kije kiyi wanka in Sha Allah daga yau zaki samu ki kwanta kiyi bacci za’a kai ki Side ɗin ki”.

Ummi dake gefe tayi murmushi kana tace.

“Ai dai kam muna shan hidima”.

Dariya Lalla Hafsat ta sanya tare da faɗin.

“Ai dai kam biki ne na musamman Shiyasa baki ɗaya abubuwan komai na musamman ne”.

Kallon Khausar dake zaune Ummi tayi kana tace.

“Toh tashi Kije kiyi wankan mana”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da miƙewa tashiga toilet ɗin daya ƙawatu komai fes-fes gwanin ban sha’awa kallon Bathtub ɗin da aka cikisa da ruwam haɗe-haɗen turaruka wanda tsaban turare da wasu abubuwan sirri daya sha sai da ya koma Sky blue ga wasu jan Flowes masu masifar kyau da suka ƙawata saman cike da farin ciki ta shiga tayi wanka bayan ta gama ta fito ɗauke da ƙaton Towel days sauƙa har gwiwanta tana fitowa Lalla Hafsat da kanta ta ɗauki Hand-drayea ta busar mata da gashin kanta kana ta ɗauki mayukan gashi masu kyau da turaren kai ta shafa mata su kana ta tufke mata su.

Bayan ta gama ta bata man shafawa tana shafawa a Fuskarta Lalla Hafsat kuwa da kanta ta tsugunna tana shafa mata aƙafanta ahankali  ta ɗago kai ta kalleta kana tace.

“Masha Allah wallahi skin ɗin ki yayi kyau Sosai”.

 

Sunkuyar da kai Khausar tayi ba tare da tace komaiba.

Miƙewa Lalla Hafsat tayi bayan ta gama shafa mata man ta miƙa mata wani tattausan Boxes irin na mata mai masifar taushi wanda bai wuce cinyarta ba kana ta miƙa mata Brasseir tare da cewa.

“Ki shiga Corridor ki sanya”.

Kai ta gyaɗa tare da karɓa tashiga Corridor ta Sanya.

Bayan ta saka Lalla Hafsat ta zaro wasu riga da wando Farare sol acikin jakar masu masifar taushi da santsi taushinsu ya wuce gaban kwatance tamkar jikin Mage haka suke.

Karɓa Khausar tayi ta saka.

Wani irin masifar amsarta kayan yayin da manyan Hips ɗinta suka baje aciki tamkar dan ita akayi su.

Kunya ce ta kama Khausar ganin yanda wanda ya kamata Hips ɗin ta suka baje aciki.

 

Wani Lifaya mai masifar kyau da taushi Jaa mai ratsin baƙi-baƙi kana shara-shara ne Lalla Hafsat ta warware tare da naɗawa Khausar sosai Khausar tayi wani kyau na ban mamaki ga yalwataccen sumanta da yasha gyara kana Lalla Hafsat ta jera mata wasu fulawowi masu kyau da tsari kana ta sa mata wani siririn sarkan Gwal da ɗan kunnensa sirara marasa nauyi zaunar da ita tayi abakin gado kana ta miƙa mata Kaskon turaren wuta.

Atake Khausar ta shiga baza ƙamshi kai kace A Company turare aka sanyata wasu turaruka kusan kala biyar masu sanyin ƙamshi Lalla Hafsat ta kuma fesa mata.

Tana gamawa Rahma na shigowa  idanunta akan Khausar tace.

“Wowww Masha Allah Lalla Hafsat kin yiwa ƙaninki shiri irin wannan tanadi duk Yah Aleey ake yiwa?”.

Murmushi Lalla Hafsat tayi kana tace.

“Ba dole ba ɗan ƙaninmu munefa mafi soyuwa a garemu ai dele mu nema masa farin cikinsa mutu masa duk abinda zai sashi farin cikin duniya”.

 

Da sauri Khausar ta rumtse idanunta sani tsinkewar da zuciyarta tayi tare  bugawa ya bada sautin bu-bu-gum wani irin tsoro ne ya ka mata.

Matsawa kusa da ita Rahma tayi ta manna kumatunta dana Khausar tayi musu selfie.

Murmushi Khausar tayi wanda ya sake ƙawata kyawun fuskarta.

 

Cikin sakin fuska da ƙaunarta Rahma tace.

“Matar yaya dan Allah akular mana da ɗan Uwan mu asashi farin ciki akwantar mishi da hankali asama mishi nutsuwa da jin daɗi”.

Ware idanu Lalla Hafsat tayi kana ta riƙe haɓa tare da cewa.

“Lalle Rahma yaushe kika fanɗare kika zama haka?”.

Murmushi tayi tare da langwaɓar da kai kana tace.

“Ai gaskiya ne Lalla Hafsat ina faɗa mata ne ta kula da Yah Aleey saboda gwara ta sani shi ɗan gata ne ɗan lelenmu ne muna sonshi fiye da yanda muke son kanmu”.

Khausar Kam wani irin tsinkewar zuciya da tsoro na ya mamaye zuciyarta.

Asma’u da bata wani daɗe da shiga ba ta kalli idanun Khausar cikin sauri ta ƙunshe dariyar ta.

 

Jakadiya ce ta kalli Lalla Hafsat kana tace.

“Hafsat kije ki duba kigani idan sun gama shiri sai muje mu kaita”.

Kai Lalla Hafsat ta gyaɗa tare da faɗin.

“Toh shikenan”

Kana ta fice ta sauƙa ƙasa kai tsaye Sashen dasu Moddibo suke ta shiga.

Zaune ta samu Ibraahim, Zakariyya, Dr Jameel suna zaune a falon.

Ibraahim na ganinta yace.

“My Aunty”.

Kafaɗarsa ta dafa tare da shafa sajen fuskarsa tace.

“Ɗan Uwana kaima gaba ɗaya abirkice kake agama dai kaima ka samu hutu kowa ma ya huta”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Ai bana ma jin gajiyar My Aunty saboda farin ciki na da kuma kwanciyar hankali na Inga komai na ɗan uwana ya kan kama”.

Murmushi tayi tare da kallon Dr Jameel da yake faɗin.

“My Aunty kwana biyu”.

Murmushi tayi kana tace.

“Lafiya lau”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Ya jikin Rahma?”.

Tana gyara tsayuwar ta tace.

“Ai tunda kazo ka bata magani alhamdulillah jiki yayi sauƙi sai iyayi take zubawa”.

Numfashi ya fesar kana yace.

“Toh Alhamdulillah”.

Juyawa tayi tare da mayar da kallonta kan Zakariyya dake cewa.

“Ke Ni baza ki gaishe Ni bane?”.

Ware idanunta tayi tana kallonsa fuskarta ɗauke da murmushi tace.

“Wai kai kam ka manta nice babba akan ka wai?”.

 

Zamansa ya gyara yana murmushin yace.

“Ni duk shekarun da kike bani kura ya cinye sa”.

“Uyum yayi kyau”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“My Aunty nima fa naga Matar Aure acikin wa’annan ƴan Uwan Amarya”.

 

Dariya tayi kana tace.

“A’a Alhamdulillah barkanmu gauraye zasu ragu”.

Dr Jameel dake latsa wayarsa yayi dariya tare da cewa.

“Zako su ragu kam In Sha Allah ku shirya biki kam ma ina ga biyu zakuyi lokaci ɗaya”.

 

Cikin yanayin ƙaunarsu da sabo Lalla Hafsat tace.

“A lallai kam Masha Allah Abu yayi kyau”.

Kallonta ta mayar kan Ibraahim kana tare da faɗin.

“Ina Aleeyu?”.

Yana kallon ƙofar bedroom din yace

“Tun da muka dawo sallama Isha’i yana daki ko abinci ma bai ci ba”.

Da damuwa tace.

“Subhanallah lafiyarsa amma”.

Ajiyar zuciya Dr Jameel ya sauƙe tare da cewa.

“Wai baya jin daɗi ne”.

Cikin sauri ta nufi bedroom ɗin abakin ƙofa ta tsaya tayi sallama.

Jin Sallamar ta yasa Moddibo ya miƙe ya zauna agefen gadon kana ya amsa mata Sallamar.

Jin ya amsa yasa ta shiga kana ta tsaya agefensa tana kallonsa.

 

Ahankali ya ɗago kansa ya kalleta.

Tana gyara tsayuwar ta tace.

“Ya dai Aleeyu lafiya kam?”.

Kai ya gyara tare da faɗin.

“Um lafiya bakomai”.

 

“Kuma Dr Jameel yace min haka jin daɗi”.

Ta faɗa tana nazartan yanayin sa.

Numfashi ya fesar kana yace.

“A’a Lafiya ta ƙalau kawai gajiya ne na gaji ina so in dan huta ne”.

 

“Ayyah sannu In Sha Allah zaka huta yanzu tashi kashiga kayi wanka zan bawa Ibraahim kayan da zaka sa zai kawo maka”.

Saurin kallonta yayi kana yace.

“Toh kuma yanzu ma wani abu za’a yi ne da sai an kawo min kayan da zansa na daban?”.

Kai ta girgiza tare da cewa.

“A’a ba wani abu kawai zaka koma Side ɗin ka inda zaka zauna ne saboda asama zaku zauna ɗaya gefen da suke tunda Side biyu ne dan can aka shirya muku”.

Numfashi yaja tare da gyada mata kai ya rasa me yake tunawa aranshi ya kuma gaza gane yanayinma da yake ciki.

Har ta juya ta fita ta isa bakin ƙofar ta tsaya tare da kallonsa ganin yana zaune tace.

“Dan Allah kayi haƙuri kayi sauri ka tashi ka shiga wanka”.

Kai ya gyaɗa tare da miƙewa ya shiga toilet ɗin yayi wanka.

 

Lalla Hafsat na fita ta kalli Ibraahim da suke hira kana tace.

“Yawwa Ibraahim zo muje ka karɓo masa kayan da zaisa.

Kallonta yayi tare da cewa.

“Ai Lalla Khadijah ma ta kawo kayan gasunan harda tsaraba waɗannan womers ɗin nace nakune ai a’a kada mu taɓa na amarya da angone in mun tashi tafiya muje da dasu abincinsu ne”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe da faɗin.

“Yawwa Alhamdulillah dama inata tunanin kar an manta da girkin”.

Kana ta fice.

Ibraahim kuwa sai da ya dai daici Moddibo ya fito kafin ya miƙe ya kai masa kayan tare da faɗin.

“Yah Aleey ga kayan”

 

Karɓan kayan Moddibo yayi da mamaki ganin Jamfofine farare ƙal da gare irin na matasan zamani yayin da yake ƙamshi ahankali yace.

“Wannan kayan fa daga ina?”.

 

Dariya Ibraahim yayi tare da cewa.

“Innayi ce wai tazo dasu tace duk ranan da zaka tare su zaka sa”.

Wani lallausan murmushi ya saki aransa yace.

“Ayyah Innayi kamar kinsan su nake bukatar sawa”

Anutse ya sanya kayan wani irin masifar kyau yayi na ban mamaki kamar asace sa agudu yayin da ya ɗauki hula Sky blue da rastin fari yasa haka zalika takalmin ma Sky blue da rastin fari kyawun da yayi sam bazai misaltuba…

Turaruka Dr Jameel ya ɗauka sun kai kala uku ya riƙa fesa masa.

Ahankali Moddibo ya kallesa tare da cewa.

“Wai kai kam mura kake son sakani?”.

 

Dr Jameel na cigaba da fesa masa yace.

“A’a gyaraka dai kawai zanyi dan kaji daɗin yanayin”.

Numfashi Moddibo ya fesar tare da faɗin.

“To ai turaren nan yayi yawa”.

Ware idanu Dr Jameel yayi yana cigaba da fesa masa yace.

“Waya faɗa maka ƙamshi yana yiwa Ango yawa aishi ƙamshinsa baya yawa”.

 

Falo suka fito Ibraahim ya ɗauki wayarsa yayi kira jin an ɗaga yasa yace.

“Ya kun gama kai musu kayan ne?”.

Daga ɗaya bangaren akace.

“Eh angama kai musu duk an shirya wa Moddibo nashi a Siff ɗinsa”.

Daga nan ya dauki wamers nan kana suka fito.

Ahankali suka fita suka fara haura step ɗin daya haura sama step ɗin ya rabu kashi biyu ɗaya ya kwanta ta gefen dama ɗaya ta gefen hagu.

Gefen dama suka bi sunyi tafiya mai tsawo akan step ɗin daya kwanta kafin suka isa wani Corridor suna shiga Corrido ƙofan farko Ibraahim ya buɗe ƙofan falon tare da cewa.

“Yah Aleeyu Bismillah ka ga Side din Auntyna ɗin”.

Masha Allah falone Mai masifar kyau da tsari kujerune set biyu ne Pinch and white ga wani madaidaicin center table  atsakiyar falon samansa anyi masa ado da wani glass Mai ƙayatarwa komai na cikin falon Pinch and white ne wasu irin Cottons ne masu masifar taushi da sheƙi ajikin window haka zalika Karfet dake malale ƙasan ɗakin shima Pinch ne da ratsin fari yayin da ɗakin ke fitar da wani sihirtaccen ƙamshi.

Sosai suka taba kyau da tsaruwan sashen.

Ibraahim na murmushi ya kalli Moddibo tare da cewa.

“Yah Aleey kai kuma ga naka agaba”.

Ya faɗa tare da nuna masa wani ƙofa dake cikin falon corridor wanda sai In dai zai shiga ko fita to dole sai ya bi ta bakin ƙofar falon Khausar dun yayin da window bedroom ɗin ta ke gab  da window  falonshi.

Kana falonshi na ɗauke da 2 bedroom daga can Corridor kuma sauran window ne sai kuma wani 1 bedroom daga baya wanda wanda yake fuskantar ƙofar corridor bisa alamu ɗakin hadimai ne.

 

Suna shiga sahensa ya lumshe idanu komai na falonsa irin ɗaya ne dana falon Khausar Colour ne kawai ya banbantasu danshi komai nasa fari ƙalll ne babu sirkin komai sai wani Masifeffen ƙamshi dake ratsa hancinsu acan bedroom ɗinsa kuwa wani round bed ne da aka ƙawatashi da wani bedsheet fari sol mai masifar taushi kana wani ma dai-dacin farin ƙyalle mai fasalin zuciya farine kal 🤍 sai dai gefen shi zagaye yake da jan zare.

sai Siff daga can gefe bedroom ɗin ba wani tarkace amma yayi kyau na ban mamaki.

 

Acan ɓangaren su Khausar kuwa Lalla Hafsat Lalla Khadijah, Ashshe ce suka shiga bedroom din.

Yayin da Ummi, Hajiya Bunayya, Asiya, Innayi ke zaune Khausar na tsakiyan.

Ashshe ce ta riƙe Khausar tare da rufe mata fuskarta da Lifayan jikinta kana suka fita daga falon.

Cikin sauri Hajja Nana ta kalli Ashshe tare da cewa.

“Nima ɗin ai zanje”.

Dariya tayi tare da cewa.

“Kizo muje mana ai nan kusa ne”.

Anutse suka fita suka fara tafiya dake tsakanin da ɗan tazara sunyi tafiya kafin suka isa falon nata.

Suna shiga Falon suka fara yaba kyau da tsaruwan kowa na faɗin albarkanci bakinsa amma banda Hajiya Bunayya dake ji kamar zuciyarta zai fasa ƙirjinta ya fita saboda baƙin ciki.

 

Kai tsaye bedroom ɗin dake gefen dama suka shiga ta tare da ajiyeta akan gadon.

 

Lalla Khadijah ce ta kira Ibraahim awaya akan suzo.

Cikin nutsuwa Ibraahim, Zakariyya, Dr Jameel suka rako Moddibo kai tsaye bedroom suka wuce bayan sun gaisa.

Lalla, Hafsat Lalla Khadijah Aunty Ashshe suka bi bayansa zuwa bedroom din.

Ramaha suka samu tsaye kusa da Khausar dake zaune bakin gadon.

A hankali ta ɗaga wani dake take riƙe da shi abu kamar towel kamar ƙyalle Fari ne ƙall  mai masifar taushi sai ƙamshi yake zubawa yana naɗe cikin leda any wrapping ɗin sa kamar Heart warwareshi tayi tare da shinfiɗashi tsakiyar gadon.

 

A hankali Ashshe tayi tayi masu nuni da hannu alamar su ƙarara shigowa ɗakin.

 

Ibraahim ne ya miƙawa Asma’u warmers dake  hannunsa tare da cewa.

“Ayyah ɗan ajiyeshi a can”.

Ya ƙare mgnar yana nuna mata kan bedside durowa.

Amsa tayi tare da juyawa ta ajiye, yayinda gaba ɗaya idanunta ke kan Dr Jameel shima ɗin ita yake kallo cike da sakin fuska yace.

“Ƙanwata ya gida”.

Lumshe ido tayi sabida hatta muryasa sak na M Jameel ne.

Ummi kuwa Moddibo dake gaisheta ta kalla tare da amsawa kana tace.

“Toh babana Allah ya sanya al’khairi Allah yayi yau dai kam mun gama cika wasiyar J ɗinka, gashi kuma Allah yasa ka sake yin katari da mai kamanninsa kaga kenan Allah ya cike maka gurbin J dinka”.

Cikin wani irin sanyi mai cike da rauni Modibbo ke kallon Ummi amman ina ya gaza cewa komai.

 

Ita kuwa Khausar haka nan taji hawaye masu ɗumi na kwaranyo mata sai kuma ta fara sakin sassayyan Shesh-sheƙan kuka mai ɗan sauti,

Baki Hajja Nana ta taɓa tare da cewa.

“Ni dai wannan kukan muna furcin ya isheni kecefa da kanki kikayiwa kanki zaɓi kika fito ido da ido kika cemin Modibbo kike so in ba Modibbo ke ba wanda zaki aura, toh ai gashi an bakishi an aura miki an kawo mishi ke sannan ki tsaida koke-koke gulma ai tunda kin samu wanda kikace kinaso mgn ta ƙare tunda da bakinki kikacewa iyayenki Ni Modibbo nake to hike nan kuma gaki gashi”.

Tunda Hajja Nana ta fara mgnar Modibbo ke kallonta, sai dai jin kalmar da tai ta nanatawa cewa wai ke kikace Modibbo kikeso.

Sai ya rumtse idanunsa da masifan karfi wani irin abu yaji zeeerr ya tsirga masa da can maɗigar kanshi har zuwa kan babbar yatsarshi.

Wani irin amintaccen numfashi mai cike da yanayi na musamman ya fesar lokacin da yaji tana kuma cewa.

“Tunda kin samu Modibbon da kike so kuma ai sai ki bar idanunki su huta”.

Yah Salam shine abinda ya iya furta cikin ransa sai kuma kalmar Ba kince Modibbo kike soba da yake ta maimaitawa tamkar mai son haddace kalaman wani irin fitinenne tsalle zuciyarsa keyi da daurawa domin kalmar tazo mishi a bazata wani irin aminci nitsuwa salama gamida yaƙini yake ji yana rufeshi.

 

Ita kuwa Khausar wani irin kunya haɗi da takaicin ne yasata sakin sassayyan kukan sabida yadda Hajja Nana ta tsinkata gaban Modibbo, domin duk yayunshi sai murmushin jin dadi suke. Ummi kuwa kai kawai ta jinjina dan lamarin Hajja Nana sai shiru.

 

cikin sanyi Innayi ta kalli Ummi tare da cewa.

“Ai Abban Jameel yace min in Sha Allah zai mishi dukan bayanin”.

Ita dai Hajja Nana ƙwaffa tayi tare da juyawa tana dube-dube ba tare da tace ko ƙalaba.

 

Zakariyya kuwa cikin sanyi yace.

“Lalla Khadi mufa zamu tafi”.

Cikin sauri ta kalli Modibbo tare da cewa.

“Bismillah a buɗe fuskar amarya, taga ɗakinta”.

 

Haka nan shima kanshi yakejin yana son yaga fuskarta, a cikin wannan yanayi da har yanzu yake mamakin ya akayi aka aura mishi ita.

Ashshe ce ta kamo hannunsa tare da matsowa kusa da Khausar da shi ɗin kana mishi alamun buɗe.

 

Wani irin sassayyan numfashi ya fesar tare da sunkuyowa yaje buɗe fuskar ta.

Wani irin lumshe idanunsa yayi atake yaji bashi da buri da yawuce ganin kyakykyawan fuskanta saboda hango ƙafafunta daya sha jan lalle da yayi ganin yanda sukayi masifar kyau lalle ya amshi ƙafarta.

Ahankali ya ƙara sunkuyowa kanta tare da shaƙan daddaɗan ƙamshin da take sai kuma yasa ya tsunsa biyu ya ɗan ƙara daga Lifayan atake kyakykyawan fuskarta ya bayyana ras a gabanshi

Juyawa yayi tare da kallon Lalla Hafsat kana yai musu alamar gashi ya buɗe.

Ibraahim dake tsaye ya miƙa masa Bounch na kuɗi alamar ya mata liƙi.

Cikin nutsuwa ya karɓa kana ɗaura mata shi kan cinyata tare da ɗan kauda fuska murya can ƙasa yace.

“Ibraahim ne yace a baki”.

Ya ida maganar yanayi mata wani irin fitinennen kalo daya sa kasala rufeta.

 

Yayin da Asma’u keta faman yi musu video tana murmushi.

Shi kuwa a hankali ya ɗan tashi tsaye.

 

Lalla Hafsat ta janyo ta tare da miƙar da ita tsaye.

Tana tsayuwa akan ƙafafunta Lalla Hafsat ta bashi wasu Bounch ɗin kuɗi alamar yayi mata liƙi.

A hankali yasa hannunshi ya amsa tare da fara yaryaɗa matasu tamkar ruwan sama.

 

Ibrahim Asma’u kuwa sai hotuna sukeyi musu.

Rahama kuwa wani turare mai sassayan kanshi ne ta fara fesa musu mai fidda zaren furanni masu color daban daban.

 

Ashshe ce tayi musu alamun su fita tare da cewa.

“Allah ya baku zaman lafiya da zuriya ɗaiyiba”.

Haka yasa gaba ɗaya  suka haɗa baki wurin cewa.

“Amin Amin”. Kana duk suka fito a tare.

 

Ita kam Khausar bata san me suke cewaba, bare tasan sun fita.

.shi kuwa Modibbo sautin Shesh-sheƙan kukanta ne ke ratsa kunneshi so bai barshi yaji mgnar suba bare fitansu, sai sautin rufe ƙofar ne da yaji ya ɗan sashi juyowa ya kalli ƙofar, tuni an rufe ƙofar bisa alamu duk sun tafi.

 

Su kuwa hakanne duk sun fita, Lalla Khadijah ce karshen fita falon bayan ta kashe wutan falon kana taja ƙofar ta fita ta bi bayansu.

A corridor ta samu Kalla Hafsat na jiranta suna fita sukaja ƙofar corridor suka rufe wacce bata  sai ta ciki sai in da key a hannun mutum ko ƙasa pin ɗin ƙofar .

 

A can cikin ɗakin kuwa, wani irin maraitaccen kuka Khausar keyi mai sassayan sautin da ya fara kashe jiki da ruhi da dukkan gangan jikin Modibbo.

Yayinda kalaman Hajja Nana keyi minshi yawo akunne zuwa tsakiyar kai tamkar busan sarewa.

 

Wani irin fitinennen rauni hadi da kasalance sukayi mishi rudugun da yasa bai san lokacin da ya ware hannunshi tare da buɗe garen jikinsa dake baza sassayan ƙamshi, a hankali ya jawota jikinsa tare dayi mata wani irin sahihin rugguma dayi mata ƙawanya da garensa kana ya bata Kekkyawan masauƙi da ƙirjinsa  haɗin dayi nata cikekken GARKUWA da hannayeshi ya matseta tsam a cikin  jikinshi….

 

 

*Littafin Sakayya dai na kuɗi ne yar uwa ki biya in tura miki littafin ki karanta cikin aminci da salama ba haƙƙin kowa aka ki, 1k ne fa kacal 0661110170 Gtbank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min evidence inki ta Whatsapp no na 09097853276, in tura miki littafin Kisha karatun ki.*

 

*Dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn, masu cewa wai sun goda suga number’n nayine, ko kuma a’a bari dai in na shirya zan sake miki mgn, ko kuma yanzu dai kuɗin bai cikaba tukun sai sun cika, ko kuma a wanne gari kike, kai munyi nisa, toh in ba iyayiba ai duk nisan state da kike ba ruwan mota ba inda bazai kai mikiba, nake turawa ƴan ƙasashen wajema. Kuyiwa Allah da Manzonsa in dai in kinsan Baki shirya sayan kaya ba ku daina min mgnar ku bari sai kun shirya,kada kizo ki ɓata min lokaci a banza, wlh ni na tsani harkar karanta, duk bayani na gamayi in dai saya zakiyi ga kuɗin kaya ga account no ga numberta ai sai ki biya kawai kafin kimin mgn. Tunda dai ga alamominshi da duk illar da yakeyi na faɗi in kina dashi faƙat in babu kada ki wani zo kice min bayani dan ko kinzo iya bayanin da zan miki kenan*

Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha’awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni’ima. Buɗewar gaba, domin har budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al’ada, rashin haihuwa, domin har baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari, da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban  lissafa. Sune manyan alamomin infection.

Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni’ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya, zaki kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni’imomin ki, da sha’awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba miki magunguna GARKUWAR MA’AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau,  duk nacin oga da yi miki wasannin bazaki ji sha’awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor’s suna kira miki, ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai Maganin na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi’izinillahi ta’ala zaki rabu dashi, cutar infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma’ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya’ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER’N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki, domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce dai GARKUWAR MA’AURATA.

 

 

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

Leave a Reply

Back to top button